Almizan :Shahadar Imam Musa Alkazeem (AS) ALMIZAN: Jarida don Karuwan Musulmi

Jarida don Karuwar Musulmi       Allah zai cika haskensa ko da kafirai sun ki

ISSN 1595-4471
Juma'a 1 Zulkidah, 1426                 Bugu na 693                                



 Tunatarwa |   | Tambaya da AmsaDandalin Siyasa | Hantsi A Takaice kai tsaye | Littafai | Duniya Labari 
Tattaunawa | Labarai
Tunatarwa:Tare da Shaikh Ibrahim Zakzaky

Shahadar Imam Musa Alkazeem (AS)

SHAIKH ZAKZAKY
Malam Ibraheem Yaqoub Zakzaky H.

Masu karatu yau muna dauke ne da ci gaban jawabin da Malam Ibraheem Zakzaky ya gabatar a wajen taron Yaumu Shuhada na bana, wanda ya gabata a filin Kofar Shahidai (Doka) Zariya a kwanakin baya. In dai ana biye da mu yau muna mako na biyar kenan da soma kawo maku wannan jawabin. Mun dan dawo baya kadan don mai karatu ya ji dadin yin karatun yadda ya kamata. Kamar yadda aka saba, Musa Muhammad Awwal ne ya rubuto mana daga kaset. A sha karatu lafiya.

Ba ni da lokacin da zan yi maku dogon bayani a kan wannan. Ina so in yi maku bayanin cewa don mutum ya sani, in ma ya ga ana rikici tsakanin musulmi da musulmi, to ya tabbatar da cewa wannan rikicin, in ya bi diddiginsa ya bincika sai ya samo asalinsa daga Amerika da Isra’ila aka yiwo.

Kuma shi Bayahude burinsa shi ne ya ga ya kashe mutum, kuma yana jin dadin ya ga gawa. Ya zo a Hadisi cewa in kuka kadaita da Bayahude, daga kai sai shi, to abin da zai zo a tunaninsa shi ne ya zai yi ya kashe ka? Wato da za ku shiga tarago daya da Bayahude, in ka ga yana kallon ka, a zuciyarsa abin da yake tunani shi ne ya zai yi ya kashe ka? Wannan, hadisin Manzon Allah ya zo da wannan.

Shi yana jin dadin ya ga gawa ta musulmi. Yana kuma son ya kashe wani ma in da ba musulmi bane. Kuma bil hasali ma har a littafinsu sun rubuta suka ce wai ayar Allah ce a cikin Attaura, “ku kashe su duk cikansu, mazan ku kashe, matan ku kashe, har yaran ku kashe, duk dabbobinsu ku kashe, shanunsu ku kashe, awakinsu ku kashe, kajin ku kashe, har kwayayensu ku kashe.” Wai aya ce a cikin Attaura.

Kuma yanzu ma suna koya wa yaransu ’yan Firamare wakoki. In sun tashi daga makaranata za su koma gida, suna waka ne ana tafi. “Za mu kashe su, za mu kashe su, duk cikansu za mu kashe su, Larabawa za mu kashe su, za mu kashe su za mu kashe su.” Waka ake koya wa yaro dan karami in ya taso daga Firamare: “Za mu kashe su, za mu kashe su, duk cikansu za mu kashe su, Larabawa za mu kashe su, kowannensu za mu kashe su, jariransu za mu kashe su, matansu ma za mu kashe su, manyansu za mu kashe su, za mu kashe su za mu kashe su.” Wannan waka ake koya wa yaro.

Don ka sani in za ka zama karen Bayahude, jakin Bayahude, wanda zai yi amfani da shi ya kashe musulmi, to ka ba da kokari. Ka sani cewa ba mamaki wannan aya za ta yi aiki a kanka, domin makomarka za ta kasance tare da shi ne. Shi kuwa in ya shiga wuta ba zai fita ba. Ba a yi wuta domin musulmi ba, amma Allah(T) yana cewa “ku ji tsoron wuta wanda makamashinta mutane ne da duwatsu wanda aka yi tanadinta domin Kafirai.” Domin ba a yi tanadin wuta domin Mumini ba, amma idan mumini ya fandare shi ma sai ya bi kafirai a wajen shiga. An yi tanadinta domin su ne. Su dawwama za su yi, in suka shiga ba su fita.

To kai ka ji tsoron wannan wutar wanda aka yi domin su, in ka yi aiki domin su, ka koma makomarsu. Ka ci wuya biyu, nan kai sunanka mumini, gobe kiyama sunanka kafiri. Kuma ka fi su ma muni don sunanka munafiki. “Innal munafikina fiddarkil asfali minannari walan tajida lahum nasira.” Munafukai sune a kuryan karshe na wuta, ba kuma za ka sami mai taimakon su ba. Ba wanda zai ce, ai wannan ya yi salla ya yi hajji, ya ba da sadaka, ya taimaka wa jama’a, a ji tausayin sa. Ba wanda zai ce haka nan. Tunda ya yi aikin Yahudawa, ya taimaka masu, ya tafi makomarsu!

A irin wannan, da so samu ne, da mun zauna musamman saboda jajanta abin da ya faru ranar Laraba da ta wuce a Kazimiyya (a lokacin da Malam yake wannan bayani). Wanda Yahudancin duniya, wanda Amerika ke wa jagoranci suka dira a kan musulmi ta hanyoyi daban-daban. Na farko, hanyar harba bama-bamai daga bayan gari, wanda muka san ba wanda zai iya harba wannan in banda Amerikawa, don su suke mamaye da kasar, kuma su suke yawo da motoci da igogi a cikin garin.

Suka harba a cikin masallaci da dandazon mutane. Mutane suka fito, ana fitowa a firgice, don bama-bamai na dira a kan mutane, ana gudu, sai kuma aka bi ta gada, gadar kuma saboda turmutsutsu har ta karye kuma aka shiga harbi. Ana cikin wannan ma sai aka harba Katuhsha, wato mizayil din Katuhsha. Wanda yake za mu tabbatar sun yi amfani da wannan ne da gangan, don Katuhsha Rasha ke kerawa, kuma ’yan Hizbullah sun sha amfani da shi a kan Yahudawa. Saboda haka Katuhsha yakan ba su tsoro, kamar yana alamta cewa abin da musulmi ke harbin su da shi kenan. Amma su makamansu na MOSSAD da na Amerika wani abu ne daban, amma ran nan sai suka harba Katuhsha a kan musulmi, wato kamar mun rama, mun harbe ku da Katuhsha. Amma su Katuhshan Hizbullah ana harba ma mayakan Isra’ila ne wanda suke yakan al’ummar musulmi. Su kuwa Katuhsha din su sun harba a cikin masallaci ne a dandazon mutane masu AZA na shahadar Imam Musa (AS).

Ana cikin wannan kuma bayan wasu sun dira sun fada ruwa, gada ta karye ta zubar da wasu, sai kuma aka je asibiti aka lura wasu na mutuwa. Kuma sai aka lura cewa an ba su abinci ne mai guba, ko ruwa na sha ko wani abinci suka ci da guba, wanda yake nufin Yahudawa sun zo kenan.

To da yake aikinsu a duk sassan duniya ne, kuma tuntuni sun sa wa kasar nan ido, ba mamaki da muka ma ga yanzu ana gargadin mutanen da suka halarci wannan taro cewa su yi hankali, an ga wani karamin munafuki, kare, ya

Komawa babban shafinmu         Komawa saman wannan shafin


  | Tafsirin Alkur'ani  | Hadisai | Crescent International